DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu zai gana da Trump ba da jimawa ba, in ji Daniel Bwala

-

Fadar shugaban Nijeriya ta bayyana cewa shugaba Bola Tinubu da shugaban Amurka, Donald Trump za su gana a cikin ‘yan kwanaki masu zuwa domin tattaunawa kan zargin kisan Kiristoci a kasar.

Wannan na zuwa ne bayan kalaman Trump da suka zargi gwamnatin Nijeriya da rashin daukar mataki kan hare-haren da ake kai wa Kiristoci, inda ya kuma yi barazanar kai hari a Nijeriya da kuma dakatar da tallafin Amurka.

Google search engine

Mai ba shugaban kasar shawara Mr Daniel Bwala ya ce shugabannin biyu na da kyakkyawar alaka wajen yaki da ta’addanci, inda ya kara da cewa gwamnatin Trump ce ta amince da sayar wa Nijeriya makamai, kuma gwamnatin Tinubu ta yi amfani da damar wajen samun gagarumar nasara a yaki da ta’addanci.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawan Nijeriya za ta tattauna da shugaba Tinubu kan kalaman Trump

Majalisar dattawan Nijeriya ta bayyana cewa za ta gana da shugaba Tinubu da bangaren zartarwa domin tattauna batun rikicin diflomasiyya da kalaman shugaban Amurka Donald...

ECOWAS ta yi watsi da zargin Trump na halaka mabiya addinin kirista a Nijeriya

Kungiyar raya tattalin arzikin kasashen yammacin Afirka ECOWAS ta fitar da sanarwa mai dauke da watsi kan zargin cewa hare-haren ta’addanci da ke ƙaruwa a...

Mafi Shahara