DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Magoya bayan bangaren Wike sun mamaye hedkwatar PDP a Abuja

-

Wasu magoya bayan bangaren sabon mukaddashin shugaban jam’iyyar PDP, Mohammed Abdulrahman, sun mamaye hedkwatar jam’iyyar da ke Wadata Plaza, Abuja, a ranar Litinin suna rera wakokin goyon baya, tare da bukatar bangaren Umar Damagum ya bar ofis nan take.

Rahotanni sun ce rikicin cikin gida na jam’iyyar ya kara kamari bayan dakatar da sakataren jam’iyya, Sanata Samuel Anyanwu, da lauya Kamaldeen Ajibade na tsawon wata guda, abin da ya haifar da kafa sabon bangare karkashin Abdulrahman.

Google search engine

A daya bangaren, magoya bayan ministan babban birnin tarayya, Nyesom Wike, sun gudanar da taro a wani wuri daban inda suka sanar da dakatar da Damagum da kwamitinsa.

Jami’an tsaro sun bazu a wurin domin hana tashin hankali yayin da bangarorin biyu ke kokarin kwace ikon ginin jam’iyyar, inda bangaren Abdulrahman ya mamaye ofishin shugaban jam’iyya na kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Hukumar Tarayyar Turai ta yi Allah-wadai da haramta biza da Amurka ta yi wa wasu Turawa

Tarayyar Turai, tare da ƙasashen Faransa da Jamus, sun yi kakkausar suka ga matakin Amurka na haramta biza ga wasu ’yan Turai da ke yaki...

Shugaba Tinubu ya yi kira ga hadin kai da hakuri a tsakanin addinai a cikin sakon taya murnar bikin Kirsimeti

Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya yi kira ga ’yan Nijeriya da su rungumi haɗin kai, juriya da zaman lafiya tsakanin mabiya addinai, yana mai cewa...

Mafi Shahara