DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Rikicin PDP na kara yin kamari yayin da bangarorin Damagum da Anyanwu ke shirin shiga ofishin jam’iyyar a lokaci guda

-

Da yiyuwar kara samun rikici a jam’iyyar PDP yayin da bangarorin shugaban jam’iyya Umar Damagum da sakatare Samuel Anyanwu ke shirin komawa aiki a ofishin jam’iyyar na kasa da ke Wadata Plaza, Abuja, a yau Litinin.

A ranar Asabar, bangaren Damagum ya gudanar da taro a Legacy House da ke Maitama, yayin da bangaren Anyanwu kuma ya yi nasa taron a ofishinsa da ke Wuye a Abuja.

Google search engine

Wata majiya daga jam’iyyar ta shaida wa Daily Trust cewa duka bangarorin biyu na shirin yin aiki a ofishin jam’iyyar guda, abin da ke haifar da fargaba a tsakanin ma’aikata na jam’iyyar.

Majiyar ta kara da cewa bangaren Nyesom Wike na kokarin jan hankalin wasu mambobin kwamitin gudanarwa domin samun rinjaye a cikin jam’iyyar, lamarin da zai iya haddasa sabon rikici idan duka bangarorin suka hadu a ofishin a yau.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shugaba Tinubu ya umurci karin jami’an tsaro a jihar Borno biyo bayan harin da aka kai a masallaci – Kashim Shettima

Mataimakin Shugaban Nijeriya, Kashim Shettima, ya ce Gwamnatin Tarayya ta tura ƙarin rundunonin tsaro na musamman zuwa Maiduguri, Jihar Borno, domin kamo waɗanda suka kai...

Kungiyar kwadago ta bukaci ‘yan Nijeriya da su yi watsi da dokokin harajin da aka gurbata

Kungiyar Kwadago ta Nijeriya (NLC) ta bukaci ’yan Nijeriya da su ƙi duk wata dokar haraji da aka ce an sauya ko an yi mata...

Mafi Shahara