DCL Hausa Radio
Kaitsaye

China ta gargadi Amurka game da yi ma Nijeriya barazana da katsalandan

-

Gwamnatin kasar China ta nuna goyon bayanta ga Shugaba Bola Tinubu, tana mai gargadi ga kowace kasa da ke tsoma baki cikin harkokin cikin gidan Nijeriya.

Mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar, Mao Ning, ta bayyana haka ne a martani ga barazanar shugaban Amurka, Donald Trump, wanda ya zargi gwamnatin Nijeriya da kisan Kiristoci.

Google search engine

Trump ya ce zai dauki matakin soja da kuma katse tallafin Amurka idan gwamnatin Tinubu ta kasa shawo kan matsalar, amma kasar China ta ce irin wannan barazana ba ta dace da dangantakar kasa da kasa ba.

Mao Ning ta kara da cewa Sin na goyon bayan Nijeriya wajen tafiyar da mulkinta bisa tsarin da ya dace da yanayin kasar, tare da yin watsi da duk wani yunkurin amfani da addini a matsayin dalilin tsoma baki kamar yadda jaridar Daily Trust ta wallafa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An fitar da jihohi 4 a Gasar Kokawar Nijar ta 2025

Kwana na uku da fara gasar kokawar gargajiya a Nijar tuni an yi waje da jihohi hudu daga cikin takwas na kasar daga jerin wanda...

Ya kamata a canza salon yadda ake yakar ‘yan bindiga a Nijeriya

Daga: Farfesa Usman Yusuf Litinin : 22 Disamba 2025 Ban taɓa gudu ko ja da baya ba ko nuna wata fargaba wajen bayyana matsayina a kan yaƙin...

Mafi Shahara