DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Amurka ta mayar wa China da martani kan gargadin harin soja a Nijeriya

-

Wani ɗan majalisar dokokin Amurka, Riley Moore, ya caccaki China saboda gargadin da ta yi wa Washington kan yiwuwar harin soja a Nijeriya bisa zargin kisan Kiristoci, yana mai cewa Beijing ba za ta tsoma baki a siyasar Amurka ba.

Moore ya goyi bayan shugaba Donald Trump, yana mai cewa Amurka na da nauyin kare Kiristoci masu fuskantar zalunci, kuma ya zargi China da rashin gaskiya kan batun ‘yancin dan Adam, yana cewa ba za a karɓi nasiha daga “gwamnatin kama-karya” ba.

Google search engine

China ta gargadi Amurka da ta daina tsoma baki a harkokin tsaron Nijeriya, inda ta bayyana goyon bayanta ga gwamnatin Nijeriya.

Sai dai gwamnatin kasar China, ta gargaɗi Trump da ya mutunta ikon da ‘yancin Nijeriya, tare da kauce wa duk wani yunkurin tura sojojin Amurka zuwa ƙasar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An fitar da jihohi 4 a Gasar Kokawar Nijar ta 2025

Kwana na uku da fara gasar kokawar gargajiya a Nijar tuni an yi waje da jihohi hudu daga cikin takwas na kasar daga jerin wanda...

Ya kamata a canza salon yadda ake yakar ‘yan bindiga a Nijeriya

Daga: Farfesa Usman Yusuf Litinin : 22 Disamba 2025 Ban taɓa gudu ko ja da baya ba ko nuna wata fargaba wajen bayyana matsayina a kan yaƙin...

Mafi Shahara