DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ci-gaban tattalin arzikin Nijeriya bai kawo saukin rayuwa ga ‘yan kasar ba – Sanusi Lamido Sanusi

-

Mai Martaba Sarkin Kano, Muhammadu Sanusi II, ya gargadi cewa ci-gaban tattalin arzikin Nijeriya ba ya fassaruwa zuwa ingantacciyar rayuwa ga ’yan ƙasar.

Sanusi ya bayyana hakan ne a wani taron kasa da kasa na Afirka kan kudin Musulunci da aka gudanar a Legas, inda ya ce ƙididdigar ci-gaban tattalin arziki da hauhawar farashi ba su nuna ainihin halin da talakawa ke ciki ba.

Google search engine

A cewarsa, duk da cewa GDP na ƙaruwa, idan ya takaita ne ga wasu kawai, yawancin jama’a za su ci gaba da fama da talauci.

Sanusi ya shawarci cibiyoyin kuɗin Musulunci da su mai da hankali wajen tallafawa kananan ’yan kasuwa, manoma da ma’aikata a yankunan karkara, yana mai cewa hakan ne kaɗai zai tabbatar da ingantacciyar rayuwa ga jama’a.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Cristiano Ronaldo zai yi ritaya daga kwallon kafa nan ba da jimawa ba

Shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na ƙasar Portugal, Cristiano Ronaldo, ya bayyana cewa zai yi ritaya daga wasa nan ba da jimawa ba, yana mai...

Gwamnatin Nijeriya ta mayar ma Amurka da martani kan kalamanta ga kasar

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa gwamnatin Amurka ta yi kuskuren fahimtar hakikanin matsalolin tsaro a kasar. Ministan yada labaran Nijeriya, Mohammed Idris, ya ce gwamnatin Nijeriya...

Mafi Shahara