DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya ta mayar ma Amurka da martani kan kalamanta ga kasar

-

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa gwamnatin Amurka ta yi kuskuren fahimtar hakikanin matsalolin tsaro a kasar.

Ministan yada labaran Nijeriya, Mohammed Idris, ya ce gwamnatin Nijeriya ta damu da yadda Amurka ta yi hanzarin fitar da wannan matsayi bisa bayanan da ba su da tushe. Ya ce matsalolin tsaro a Nijeriya sun shafi Musulmai da Kiristoci baki É—aya, ba wai rikicin addini ba ne.

Google search engine

DCL Hausa ta ruwaito cewa Ministan ya jaddada cewa rikicin manoma da makiyaya a Plateau da Benue ya samo asali daga tsoffin matsaloli da canjin yanayi da fari suka haifar da ƙara taɓarɓarewar. Ya ƙara da cewa gwamnati tana ƙarfafa haɗin kai da ƙasashen duniya, ciki har da Amurka, don kawo ƙarshen ta’addanci a yankin Sahel da Nijeriya baki ɗaya.

A cewarsa, hadin gwiwar da ke tsakanin Nijeriya da Amurka ya haifar da samun jiragen Super Tucano da ake amfani da su a yaƙin ta’addanci, tare da shirin karɓar sabbin jiragen yaƙi na AH-1Z Viper domin ƙarfafa rundunar sojojin sama.

Hakazalika, ya ce gwamnatin Tinubu tana bin duk hanyoyin diflomasiyya da siyasa don gyara kuskuren fahimtar da gwamnatin Amurka ta yi, tare da tabbatar da cewa ’yancin addini da rayuwar kowane ɗan ƙasa za su kasance a ƙarƙashin kariya da doka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Cristiano Ronaldo zai yi ritaya daga kwallon kafa nan ba da jimawa ba

Shahararren ɗan wasan ƙwallon ƙafa na ƙasar Portugal, Cristiano Ronaldo, ya bayyana cewa zai yi ritaya daga wasa nan ba da jimawa ba, yana mai...

PDP ta kafa kwamitin sulhu tsakanin bangarorin da ke rikici a jam’iyyar

Kwamitin amintattu na jam’iyyar PDP ya kafa kwamiti na musamman domin sasanta dukkan bangarorin da ke cikin sabani kafin babban taron zaben shugabanni na kasa...

Mafi Shahara