DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Muna bibiyar barazanar hari da Amurka ke yi ma Nijeriya sau da kafa – Gwamnatin Rasha

-

Gwamnatin Rasha ta bayyana cewa tana sa ido sosai kan rahotannin da ke nuna yiwuwar Amurka ta kai farmaki a Nijeriya, kamar yadda mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar, Maria Zakharova, ta tabbatar a ranar Juma’a.

A yayin taron manema labarai a Moscow, Zakharova ta ce Rasha tana kira ga Washington da sauran bangarorin da abin ya shafa da su bi doka da ka’idojin kasa da kasa wajen magance matsalar.

Google search engine

Rahotanni sun nuna cewa a ranar 1 ga watan Nuwamba, shugaban Amurka Donald Trump ya umurci Pentagon da ta tsara matakan soja da za a iya dauka a Nijeriya don kare al’ummar Kiristoci daga kungiyoyin ta’addanci kamar yadda jaridar TRT Afrika ta wallafa.

Sai dai gwamnatin Nijeriya ta ce ba ta lamuntar wariyar addini, inda ministan harkokin wajen kasar, Yusuf Tuggar, ya jaddada cewa tsarin mulkin Nijeriya yana tabbatar da ‘yancin addini da bin doka da oda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babu adawa a jihar Plateau a zaben 2027 – Caleb Muftwang

Gwamnan Jihar Plateau, Caleb Manasseh Mutfwang, ya bayyana cewa zuwa zaben 2027 jam’iyyarsa ba za ta samu adawa a jihar ba. Ya fadi hakan ne...

Obasanjo ya musanta rubuta sanarwar mutuwarsa

Tsohon Shugaban Nijeriya, Olusegun Obasanjo, ya musanta wani rubutu da ke yawo a kafafen sada zumunta da ke ikirarin cewa ya fitar da sanarwar mutuwarsa. Rubutun...

Mafi Shahara