Gwamnatin Rasha ta bayyana cewa tana sa ido sosai kan rahotannin da ke nuna yiwuwar Amurka ta kai farmaki a Nijeriya, kamar yadda mai magana da yawun ma’aikatar harkokin wajen kasar, Maria Zakharova, ta tabbatar a ranar Juma’a.
A yayin taron manema labarai a Moscow, Zakharova ta ce Rasha tana kira ga Washington da sauran bangarorin da abin ya shafa da su bi doka da ka’idojin kasa da kasa wajen magance matsalar.
Rahotanni sun nuna cewa a ranar 1 ga watan Nuwamba, shugaban Amurka Donald Trump ya umurci Pentagon da ta tsara matakan soja da za a iya dauka a Nijeriya don kare al’ummar Kiristoci daga kungiyoyin ta’addanci kamar yadda jaridar TRT Afrika ta wallafa.
Sai dai gwamnatin Nijeriya ta ce ba ta lamuntar wariyar addini, inda ministan harkokin wajen kasar, Yusuf Tuggar, ya jaddada cewa tsarin mulkin Nijeriya yana tabbatar da ‘yancin addini da bin doka da oda.



