Mataimakin shugaban Majalisar Dattawan Nijeriya, Sanata Barau Jibrin, ya caccaki Shugaban Amurka, Donald Trump, bisa barazanar kai wa Nijeriya hari da ya yi,saboda zargin ana yi wa Kiristocin kasar kisan kiyashi.
Jaridar Punch ta rawaito cewa a cikin wani faifan bidiyo an gano Sanata Barau Jibrin na cewa furucin Trump ya saba wa dokar ƙasa da ƙasa bisa wannan kuduri da ya dauka.
Ya kuma bukaci shugaban Amurkan da ya janye kalamansa tare da bai wa Nijeriya hakuri, yana mai cewa, bai dace shugaban Amurka ya ce zai kai wa wata ƙasa hari saboda ra’ayi ba, idan akwai matsala kamata ya yi a bi ta hanyar diflomasiyya.



