DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Kano ya rattaba hannu kan bukatar samar da kwalejin Polytechnic a Gaya

-

Gwamnan Kano Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan dokar kafa kwalejin kimiyya da fasaha “Gaya Polytechnic” a wani mataki na fadada damar samun ilimin gaba da sakandare tare da inganta koyon sana’o’in zamani a fadin jihar.

Mai magana da yawun gwamnan Sunusi Bature Dawakin Tofa, ya bayyana haka ne bayan rattaba hannun da ya samu halartar shugaban majalisar dokoki ta jihar Kano, Rt. Hon. Jibril Isma’il Falgore, da mataimakin shugaban majalisar, Hon. Muhammad Bello Butubutu, wadanda suka mika kudirin.

Google search engine

Gwamnan ya ce sabuwar kwalejin za ta bai wa matasa damarmaki na koyon horo da fasaha da za su taimaka wajen bunkasa tattalin arziki, kuma wannan shine burin gwamnati wajen fadada harkokin ilimi a fadin jihar Kano.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ma’aikatan majalisa sun rufe majalisar dokokin jihar Bauchi sakamakon tsunduma yajin aiki 

Shugaban ƙungiyar ma’aikatan majalisun jihohi ta Nijeriya (PASAN) a jihar Bauchi Adamu Yusuf ne ya sanar da hakan ranar Juma’a, bisa bin umarnin shugabancin ƙungiyar...

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Hassan ta umarci a binciko dalilin rikicin da ya faru a lokacin zaben kasar

Shugabar Tanzania Samia Suluhu Hassan ta umarci a binciko dalilin rikicin da ya faru a lokacin zaben kasar da ta sake yin nasara. Wannan mataki ya...

Mafi Shahara