DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga sun halaka jigo a jam’iyyar APCn jihar Zamfara

-

Wasu da ake zargin ’yan bindiga ne sun halaka wani jigo a jam’iyyar APC a jihar Zamfara, Alhaji Umar Moriki da safiyar ranar Asabar.

Gidan talabijin na Channels, ya ruwaito cewa lamarin ya faru ne a kan hanyar Gusau zuwa Tsafe, kusa da garin Fegi a karamar hukumar Tsafe, yayin da Marigayin ke tafiya daga Gusau zuwa Kaduna.

Google search engine

A wata sanarwa da sakataren yaɗa labaran APC a jihar Zamfara Yusuf Idris ya fitar, jam’iyyar ta bayyana rasuwar Marigayi Moriki a matsayin babban rashi, inda ta ce ya halarci taron shugabannin jam’iyya da karamin ministan tsaro Bello Matawalle ya jagoranta kafin aukuwar harin.

Marigayi Moriki ya taɓa rike mukamai da dama, ciki har da mataimakin shugaban karamar hukumar Zurmi da mai bai wa gwamna shawara kan hasken wutar lantarki a yankunan karkara, kazalika ya yi takarar kujerar majalisar wakilai ta Zurmi/Shinkafi a zaben 2023.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Jam’iyyar PDP ta kori su Wike daga cikinta

Jam'iyyar PDP mai hamayya a Nijeriya ta bayyana korar ministan birnin Abuja Nyesom Wike da wasu 'ya'yanta daga cikinta. Tsohon mataimakin shugaban jam'iyyar na yankin kudancin...

Wa’adina na biyu zai zama mai tsauri ga masu tu’ammali da miyagun kwayoyi – Buba Marwa

Shugaban hukumar yaki da sha da fataucin miyagun kwayoyi ta Nijeriya NDLEA, Janar Buba Marwa (rtd), ya bayyana cewa wa’adinsa na biyu zai zama mafi...

Mafi Shahara