DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Barayin daji sun hallaka mutane 3 tare da sace akalla 64 a jihar Zamfara

-

’Yan bindiga sun hallaka mutane uku tare da sace akalla 64 a Fegin Baza da ke Tsafe, jihar Zamfara. Mata da yara na cikin wadanda aka yi garkuwa da su, sannan mutane hudu sun jikkata.

Jaridar Daily Trust ta ruwaito cewa, daga cikin wadanda aka kashe har da jigo a jam’iyyar APC, Umaru Moriki, wanda aka harba a kan hanyar Gusau zuwa Tsafe. Shaidun gani da ido sun ce maharan sama da 30 ne dauke da bindigogi a kan babura.

Google search engine

Harin ya faru kwana guda bayan ziyarar ministan tsaro Bello Matawalle, wanda ya sanar da turo sabbin sojoji tare da alkawarin murkushe ’yan bindiga.

Zamfara na ci-gaba da fama da hare-hare a kauyuka da hanyoyi, lamarin da ya tilasta dubban mutane barin gidajensu bayan garkuwa, kashe-kashe da barna sun yi kamari.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawa ta bukaci a dauki matasa aikin tsaro domin magance matsalar tsaro

Majalisar dattawan Nijeriya, ta nuna damuwa kan tabarbarewar tsaro a ƙasar, tana kira ga shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya amince da daukar matasa akalla...

Matukar dimokradiyya ta gaza a Nijeriya sai ya shafi fadin Yammacin Afrika – ECOWAS

Kungiyar tattalin arzikin kasashen Yammacin Afrika, ECOWAS, ta gargadi cewa duk wani rauni da dimokuradiyya ta samu a Nijeriya zai yi sanadin rushewar tsarin a...

Mafi Shahara