DCL Hausa Radio
Kaitsaye

PDP bangaren Wike sun kira taron gaggawa na shugabanni da ƴan kwamitin amintattu na jam’iyyar

-

Bangaren jam’iyyar PDP da ke goyon bayan ministan Abuja, Nyesom Wike, ya sanar da cewa za a gudanar da taron gaggawa na kwamitin amintattu da na zartaswa na jam’iyyar a ranar Talata, 18 ga watan Nuwamba, 2025, a hedikwatar jam’iyyar da ke Wadata Plaza, Abuja.

A cikin sanarwar da sakataren Jam’iyyar na bangaren Wike, Samuel Anyanwu, ta nuna wadda mai taimakawa ministan wajen yada labarai, Lere Olayinka, ya wallafa, taron amintattun zai fara da misalin 11 na safe, yayin da na zartaswa zai biyo baya da karfe 2 na rana.

Google search engine

Sanarwar ta ce halartar manyan jiga-jigan jam’iyyar yana da muhimmanci domin tattaunawa kan muhimman batutuwa, musamman bayan da PDP a taronta na kasa da aka yi a Ibadan ta kori Wike, Anyanwu, Ayo Fayose, Kamaldeen Ajibade da wasu shugabanni bisa zargin cin amanar jam’iyya.

Korarsu ta biyo bayan kudirin da Bode George ya gabatar, Samaila Buga na PDP Bauchi ya mara wa baya, sannan gwamna Bala Mohammed ya sanya wa kwamitin muryar amincewa wadda ta nuna sahalewar wakilai kan hukuncin share baragurbin cikin jam’iyyar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun saurari kiran da aka ba da umarnin kama ni bayan wani ya yi kutsen wayar Ribadu – El-Rufai

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya ce ya saurari wata tattaunawar waya da ya danganta da Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (NSA),...

El-Rufai ya zargi gwamnatin Tinubu da hannu a yunƙurin sanya Kwankwaso cikin jerin takunkumin Amurka

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya yi zargin cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na iya kasancewa a bayan yunƙurin dan Majalisar Dokokin Amurka,...

Mafi Shahara