DCL Hausa Radio
Kaitsaye

PDP tsagin Wike ta kori Bala Muhd da Dauda Lawan, gwamnonin Bauchi da Zamfara

-

Jam’iyyar PDP ta kara shiga wani sabon rikici a ranar Talata bayan bangaren kwamitin zartaswa da ke goyon bayan ministan Abuja, Nyesom Wike, ya tabbatar da korar gwamna Oyo, Seyi Makinde, da na Bauchi, Bala Mohammed da kuma na Zamfara, Dauda Lawal.

Kamar yadda sanarwar da Sanata Sam Anyanwu ya karanta ta bayyana, zaman NEC da aka yi a Wadata Plaza ya kuma kori tsohon shugaban kwamitin amintattu, Adolphus Wabara, Bode George da sabon shugaban jam’iyyar da aka zaba Kabiru Turaki, SAN.

Google search engine

Sanarwar ta ce matakin ya biyo bayan babban taron PDP na Ibadan da ya haifar da sabani, lamarin da ya janyo arangama bayan bangarorin biyu sun shirya zaman NEC da BoT a sakatariyar jam’iyyar.

PDP ta kuma rushe shugabanni a jihohi shida tare da umartar kafa rikon kwarya, sannan ta amince da fara hukunci kan wasu jiga-jigan jam’iyya bisa zargin karya doka da bata sunan jam’iyya kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar dattawa ta bukaci a dauki matasa aikin tsaro domin magance matsalar tsaro

Majalisar dattawan Nijeriya, ta nuna damuwa kan tabarbarewar tsaro a ƙasar, tana kira ga shugaban ƙasa Bola Tinubu da ya amince da daukar matasa akalla...

Matukar dimokradiyya ta gaza a Nijeriya sai ya shafi fadin Yammacin Afrika – ECOWAS

Kungiyar tattalin arzikin kasashen Yammacin Afrika, ECOWAS, ta gargadi cewa duk wani rauni da dimokuradiyya ta samu a Nijeriya zai yi sanadin rushewar tsarin a...

Mafi Shahara