DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tsare-tsaren gwamnati na da manufar yaki da talauci a tsakanin matasa – Shugaba Tinubu

-

Shugaban Nijeriya, Bola Tinubu ya bayyana cewa manufofin tattalin arziki da na gyare-gyaren hukumomin gwamnati suna nufin bai wa matasa kwarewa da ilimi mai inganci domin su iya fafatawa a duniya da kuma tabbatar da makomarsu ta hanyar ci-gaban ilimi.

Tinubu ya yi wannan bayani ne a ranar Litinin yayin da yake karbar Duke na Edinburgh, Prince Edward, a Fadar shugaban Nijeriya, Abuja kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Google search engine

A cewarsa, batun matasa zai kasance gaba-gaba a taron G-20 da za a gudanar wannan makon, inda ya kara da cewa manufofin gwamnati sun mayar da hankali kan yawan jama’a da bunkasa kwarewa don habaka tattalin arziki.

Hakazalika, ya jaddada cewa sabon shirin bayar da rancen dalibai wani muhimmin mataki ne na fadada damar samun ilimi ga matasa, inda ya ce gwamnati na amfani da kyawawan dabaru wajen samar da kwarewa a fannoni da dama, domin inganta rayuwar matasa da ci-gaban kasa.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Babban hafsan sojin kasa ya umurci sojoji da su tsaurara wajen ganin sun ceto dalibai mata da aka sace a jihar Kebbi

Babban hafsan rundunar sojin kasa, Laftanar Janar Waidi Shaibu, ya umarci dakarun Operation Fansan Yamma da su matsa kaimi wajen ceto daliban GGCSS Maga da...

’Yan bindiga sun sace fasinjoji shida a hanyar Ogobia–Adoka a Benue

’Yan bindiga sun tare wata motar haya suka tafi da fasinjoji shida sannan suka kashe direba a hanyar Ogobia–Adoka da ke ƙaramar hukumar Otukpo a...

Mafi Shahara