DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Kano ya dauki malaman lissafi 400 aiki a makarantun sakandire

-

Gwamnan jihar Kano Abba Kabir Yusuf ya sanya hannu kan takardar daukar malaman lissafi 400 a makarantun sakandiren da ke fadin jihar aiki.

 

Google search engine

Wata sanarwa da mai magana da yawun gwamnan Sanusi Bature Dawakin Tofa ya fitar, ta bayyana cewa daukar matakin wani yunkuri ne na cike gibin da ake samu a ilimin daliban jihar Kano, kamar yadda Daily Trust ta ruwaito.

 

A cewar sa, darasin lissafi shi ne ginshikin kimiyya, fasaha, kirkire-kirkire har ma da fagen injiniyanci, a don haka ya zama wajibi gwamnati ta mayar da hankali wajen inganta matakin iliminta.

 

Gwamnan ya bukaci sabbin malaman da su sanya kwarewa da mayar da hankali wajen ganin sun sauke nauyin da ya rataya a wuyansu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun saurari kiran da aka ba da umarnin kama ni bayan wani ya yi kutsen wayar Ribadu – El-Rufai

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya ce ya saurari wata tattaunawar waya da ya danganta da Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (NSA),...

El-Rufai ya zargi gwamnatin Tinubu da hannu a yunƙurin sanya Kwankwaso cikin jerin takunkumin Amurka

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya yi zargin cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na iya kasancewa a bayan yunƙurin dan Majalisar Dokokin Amurka,...

Mafi Shahara