Tsohon gwamnan jihar Kano Rabi’u Musa Kwankwaso ya yi kira ga gwamnatin Nijeriya ta da gudanar da bincike kan musabbabin ta’azzarar matsalar tsaro a wasu sassan kasar.
Cikin wani sako da ya wallafa a shafinsa na X, Kwankwaso ya yi Allah-wadai da sace ‘yan makaranta 25 da ‘yan bindiga suka yi a jihar Kebbi, bayan farmakin da suka kai.
Kazalika Kwankwaso ya nuna damuwa da sauran matsalolin tsaro da ke faruwa a jihohi irin su Zamfara da Kano, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
A hannu guda, ya bayyana kisan Birgediya Janar Musa Uba a Borno a matsayin wani bakin tabo a fagen tsaron Nijeriya, yana mai bukatar a gaggauta bincikar lamarin.



