Wani mai lalurar gani daga jihar Sokoto ya cike neman aiki a hukumar kula da shige da fice ta Nijeriya ‘Immigration’.
Daily Trust ta ruwaito yadda mutumin mai suna Umar Muhammad dan shekaru 25 ya nemi aikin, duk da cewa ya rasa idanunsa tun yana kimanin shekaru 6 da haihuwa a hannun wasu ‘yan kungiyar asiri.
Ya bayyana kwarin gwiwa da cewa akwai sabuwar doka da ta wajabtawa gwamnati bai wa masu bukata ta musamman damar neman aiki da kaso biyar.
Cikin larurar tasa, Umar ya kammala karatun NCE a Kwalejin Ilimi ta Shehu Shagari da ke Sokoto, inda yanzu haka yake karatun digiri a jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke jihar.
A baya kafin wannan lokaci dai ya taba samun takardar aiki da gwamnatin jihar Sokoto a lokacin da tsohon gwamna Aminu Waziri Tambuwal ke daf da sauka, sai dai gwamnatin yanzu ta dakatar da aikin saboda wasu dalilai, kamar yadda ya shaidawa jaridar.



