DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Wani mai lalurar gani ya cike neman aikin “Immigration” a Nijeriya

-

Wani mai lalurar gani daga jihar Sokoto ya cike neman aiki a hukumar kula da shige da fice ta Nijeriya ‘Immigration’.

Daily Trust ta ruwaito yadda mutumin mai suna Umar Muhammad dan shekaru 25 ya nemi aikin, duk da cewa ya rasa idanunsa tun yana kimanin shekaru 6 da haihuwa a hannun wasu ‘yan kungiyar asiri.

Google search engine

Ya bayyana kwarin gwiwa da cewa akwai sabuwar doka da ta wajabtawa gwamnati bai wa masu bukata ta musamman damar neman aiki da kaso biyar.

Cikin larurar tasa, Umar ya kammala karatun NCE a Kwalejin Ilimi ta Shehu Shagari da ke Sokoto, inda yanzu haka yake karatun digiri a jami’ar Usmanu Danfodiyo da ke jihar.

A baya kafin wannan lokaci dai ya taba samun takardar aiki da gwamnatin jihar Sokoto a lokacin da tsohon gwamna Aminu Waziri Tambuwal ke daf da sauka, sai dai gwamnatin yanzu ta dakatar da aikin saboda wasu dalilai, kamar yadda ya shaidawa jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Peter Obi ya bukaci matasa da su nuna kauna da kishin Nijeriya albarkacin ranar masoya

Tsohon ɗan takarar shugaban Nijeriya, Peter Obi, ya bukaci ’yan Nijeriya musamman matasa su yi bikin ranar masoya ta Valentine cikin nuna kishin ƙasa da...

Nijeriya na da damar jagorantar Afirka ta zama babbar nahiya a duniya – António Guterres

Sakatare-Janar na Majalisar Dinkin Duniya, António Guterres, ya bukaci Nijeriya ta jagoranci Afirka wajen neman sauyi a tsarin duniya, yana mai cewa ƙasar na da...

Mafi Shahara