DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Majalisar dokokin jihar Kebbi ta dakatar da shugaban karamar hukumar Fakai

-

Majalisar dokokin jihar Kebbi ta dakatar da shugaban karamar hukumar Fakai a jihar Kebbi da DCL Hausa ta yi rahoton zargin da ake yi masa na cefanar da fili da ‘transatomomi’.

Majalisar Dokokin Jihar Kebbi ta dakatar da shugaban ƙaramar hukumar Fakai, Muhammad Mahuta, bisa zargin aikata munanan ayyuka da sakaci wajen gudanar da aikinsa, biyo bayan amincewa da rahoton kwamiti na musamman da majalisar ta kafa ƙarƙashin jagorancin Salihu Dangoje, kamar yadda rahoton jaridar Punch ya nuna.

Google search engine

A cewar kwamitin, bincike ya gano zarge-zargen haɗa hannu wajen cire da kuma yunƙurin sayar da injinan wuta guda biyar, rabon gonakin gwamnati ba bisa ka’ida ba, da karya yarjejeniyar aikin gyaran madatsar Mahuta.

Kwamitin ya ce Mahuta ya bayyana musu cewa an ɗauki injinan ne domin gyara da izinin wani jami’in KEDCO mai suna Malam Nasir, wanda bai amsa gayyatar kwamitin ba.

Sai dai a ranar 14 ga Nuwamba, shugaban ƙaramar hukumar ya amsa gaban kwamitin cewa ya yi almundahanar injinan guda biyar da ake shirin sayar wa wani Alhaji Kabiru Dauda kan naira miliyan 2.5 kowanne.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Akwai gibi mai tarin yawa da muka gano cikin sabbin dokokin harajin Tinubu a Nijeriya – Kamfanin haraji na KPMG

Kamfanin haraji na KPMG, ya bayyana cewa ya gano manyan kura-kurai, a cikin sabbin dokokin haraji na Nijeriya, duk da burin da gwamnati ke da...

Za a yi zabukan ‘yan majalisar dokoki da kananan hukumomi a Benin

Kasar Benin Republic za ta gudanar da zaɓukan ’yan majalisar dokoki da na ƙananan hukumomi a ranar Lahadi, wata guda bayan wani yunkurin juyin mulki...

Mafi Shahara