DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Katsina ta rufe duk makarantun sakandare da firamare saboda barazanar tsaro

-

Gwamnatin Jihar Katsina ta bada umarnin rufe dukkan makarantu sakamakon tsananin barazanar tsaro da ake fuskanta a arewacin kasar, musamman bayan sace dalibai a Jahohin Neja da Kebbi. Kwamishinan Ilmi na Jihar ya tabbatar da hakan, inda ya ce matakin ya zama dole domin kare rayuwar dalibai da malamai.

Wannan batu ya yi karfi musamman idan aka yi la’akari da wani sabon rahoto da ya nuna cewa sama da yara 300,000 a Katsina ba sa zuwa makaranta saboda tsaro mai rauni.

Google search engine

DCL Hausa ta ruwaito cewa gwamnati na duba yiwuwar sake fasalin tsaron makarantun jihar, yayin da ake cigaba da kai hare-hare a makarantu daban-daban a arewacin kasar. Masu sharhi dai na ganin cewa rufe makarantu ka iya kare rayuka, amma hadarin da yake haifarwa ga makomar ilimi ya fi tsanani idan ba a dauki matakan gaggawa ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tsare-tsaren Tinubu na farfaɗo da martabar Nijeriya a duniya -Kashim Shatima

Mataimakin Shugaban Ƙasa, Kashim Shettima, ya ce gyare-gyaren da gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu ke aiwatarwa na sake gina martabar Nijeriya a idon duniya tare...

Gwamnatin Nijeriya na shirin dakatar da shigo da kayan tsaro daga waje

Gwamnatin Nijeriya ta yi niyyar kera dukkan makami da ake buƙata a cikin gida nan da shekara biyu zuwa biyar masu zuwa. Minista a ma'aikatar Tsaron...

Mafi Shahara