DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Binciken kwakkwafi da ake ne ya hana a gurfanar da wadanda ake zargi da daukar nauyin ta’addanci – Gwamnatin Nijeriya

-

Ministan yaɗa labarai, Mohammed Idris ya ce gwamnati ba ta gurfanar da waɗanda ake zargi da ɗaukar nauyin ta’addanci ba saakamakon binciken yana da sarkakiya, ba kuma abin da za a hanzarta shi ba ne duk da matsin lambar jama’a.

Jaridar Punch ta ruwaito Idris ya ce, ba wai da an samu jerin sunaye ne kawai za a garzaya kotu ba, yana mai cewa dole a tattara bayanai sosai kafin daukar mataki. Wannan na zuwa ne yayin da ake ƙara zargin gwamnati da rashin gaskiya kan yawaitar hare-haren tsaro.

Google search engine

Ministan ya ce gwamnatin Tinubu na aiki tukuru wajen murƙushe ta’addanci, inda ya bayyana cewa tun daga Mayu 2023 sama da ’yan ta’adda 13,500 aka hallaka, fiye da 17,000 kuma aka kama, wasu ma na fuskantar shari’a yanzu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun yi nadamar yekuwar a ba Yilwatda shugabancin APC – Kungiyar magoya bayan jam’iyyar na Arewa ta tsakiya

Kungiyar magoya bayan jam'iyyar APC a Yankin Arewa ta Tsakiyar Nijeriya ta bayyana nadamarta bayan ta dage kai da fata sai an naɗa dan yankin...

Kungiyar tarayyar Turai za ta tallafa ma gwamnatin Nijeriya da Yuro miliyan 45 don inganta fasahar zamani

Kungiyar Tarayyar Turai (EU) tare da abokan huldarta sun kaddamar da sabon mataki na hanzarta sauyin fasahar dijital a Nijeriya, yayin taron kwamitin kula da...

Mafi Shahara