DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Binciken kwakkwafi da ake ne ya hana a gurfanar da wadanda ake zargi da daukar nauyin ta’addanci – Gwamnatin Nijeriya

-

Ministan yaɗa labarai, Mohammed Idris ya ce gwamnati ba ta gurfanar da waɗanda ake zargi da ɗaukar nauyin ta’addanci ba saakamakon binciken yana da sarkakiya, ba kuma abin da za a hanzarta shi ba ne duk da matsin lambar jama’a.

Jaridar Punch ta ruwaito Idris ya ce, ba wai da an samu jerin sunaye ne kawai za a garzaya kotu ba, yana mai cewa dole a tattara bayanai sosai kafin daukar mataki. Wannan na zuwa ne yayin da ake ƙara zargin gwamnati da rashin gaskiya kan yawaitar hare-haren tsaro.

Google search engine

Ministan ya ce gwamnatin Tinubu na aiki tukuru wajen murƙushe ta’addanci, inda ya bayyana cewa tun daga Mayu 2023 sama da ’yan ta’adda 13,500 aka hallaka, fiye da 17,000 kuma aka kama, wasu ma na fuskantar shari’a yanzu.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara