Tsohon dan takarar shugabancin Nijeriya Atiku Abubakar zai yi rajista a jam’iyyar ADC a Litinan din nan tare da magoya bayansa.
Wata majiya ta tabbatar wa jaridar Daily Trust cewa an kammala dukkan shirye-shirye domin yin rajistar ta sa a unguwarsa ta Jada Ward 1, jihar Adamawa, sa’annan zai gana da shugabannin jam’iyyar a Yola.
A baya dai an samu tantama kan Atiku da Peter Obi wajen shiga ADC, duk da hadakar ‘yan adawa da suke jagoranta a jam’iyyar, wacce suke fatar neman tsayawa takarar shugabancin Nijeriya a shekarar 2027.



