DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnan Kebbi ya soki rundunar sojin Nijeriya kan yadda take yakar rashin tsaro

-

Gwamnan jihar Kebbi Nasir Idris ya nuna rashin gamsuwa da tsarin da rundunar soji ke amfani da shi wajen yakar rashin tsaro yana mai kira da a sauya dabarar aiki.

Gwamman ya bayyana haka ne a Litinin din nan lokacin da ya karɓi bakuncin ‘yan Majalisar wakilai karkashin jagorancin kakakin Majalisar Tajudeen Abbas a gidan gwamnati da ke Birnin Kebbi.

Google search engine

Jaridar Daily Trust ta rawaito gwamnan na sake jaddada bukatar yin bincike kan janye jami’an tsaro daga makarantar ta ‘yan mata ta Maga mintuna kaɗan kafin ’yan bindiga su sace ’yan mata 25.

A cewar gwamnan abin mamaki ne yadda ‘yan bindiga fiye da 500 ke yawo a babura a manyan hanyoyi ba tare da an dakatar da su ba, duk da cewa gwamnati na ba da tallafi, kayan aiki, da motoci ga jami’an tsaro.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara