DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin jihar Bauchi ta rufe dukkanin makarantun da ke fadin jihar

-

Gwamnatin jihar Bauchi ta sanar da rufe dukkan makarantu firamare, sakandare da manyan makarantu ciki har da na masu zaman kansu sakamakon matsalar tsaro.

Rufe makarantun ya biyo bayan munanan hare-hare da aka kai kwanakin nan ciki har da sace dalibai a jihohin Neja da Kebbi.

Google search engine

Haka kuma ‘yan bindiga sun halaka ‘yan sanda biyar a kauyen Sabon Sara a ƙaramar hukumar Darazo ta jihar kamar yadda rundunar ‘yan sandan jihar Bauchin ta tabbatar.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ma’aikatar Ilimi ta jihar Bauchi Jalaludeen Usman ya fitar, gwamnati ta ce rufe makarantun ya biyo bayan tattaunawa da hukumomin tsaro tare da la’akari da tsaron dalibai da malamai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara