DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin jihar Bauchi ta rufe dukkanin makarantun da ke fadin jihar

-

Gwamnatin jihar Bauchi ta sanar da rufe dukkan makarantu firamare, sakandare da manyan makarantu ciki har da na masu zaman kansu sakamakon matsalar tsaro.

Rufe makarantun ya biyo bayan munanan hare-hare da aka kai kwanakin nan ciki har da sace dalibai a jihohin Neja da Kebbi.

Google search engine

Haka kuma ‘yan bindiga sun halaka ‘yan sanda biyar a kauyen Sabon Sara a ƙaramar hukumar Darazo ta jihar kamar yadda rundunar ‘yan sandan jihar Bauchin ta tabbatar.

A cikin wata sanarwa da mai magana da yawun ma’aikatar Ilimi ta jihar Bauchi Jalaludeen Usman ya fitar, gwamnati ta ce rufe makarantun ya biyo bayan tattaunawa da hukumomin tsaro tare da la’akari da tsaron dalibai da malamai.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Makarantun Sakandire na je-ka-ka dawo za su ci gaba da karatu – Gwamnatin Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta bai wa makarantun firamare da sakandare na je-ka-ka-dawo damar ci gaba da karatu A wata sanarwa da ma’aikatar ilimi ta jihar ta...

Jam’iyyar PDP ta bukaci Shugaba Tinubu ya nemi taimako ko ya yi murabus

Jam’iyyar PDP ta na shawartar Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya nemi taimako ko ya yi murabus, sakamakon yawaitar hare haren 'yan bindiga da sace sacen...

Mafi Shahara