DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar PDP ta bukaci Shugaba Tinubu ya nemi taimako ko ya yi murabus

-

Jam’iyyar PDP ta na shawartar Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya nemi taimako ko ya yi murabus, sakamakon yawaitar hare haren ‘yan bindiga da sace sacen ɗalibai da ya addabi jihohin Arewa a kwanakin nan.

A wani taron manema labarai da jam’iyyar ta yi a Abuja, mai magana da yawunta na ƙasa Ini Ememobong ya ce sace ɗalibai a jihar Kebbi da Niger da kuma masu ibada a Kwara na nuna gazawar Gwamnatin Tinubu wajen magance matsalar tsaro.

Google search engine

A cewar sa gwamnati ta gaza aikinta na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan ƙasa, yana mai jaddada cewa idan gwamnati ta kasa wannan aiki to ga dole ta nemi taimako daga cikin gida ko wajen ƙasa.

PDP ta ce matakin rufe wasu makarantun da wasu jihohi ke yi babu inda zai kai, domin hakan kamar mika wuya ne ga ‘yan ta’adda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Makarantun Sakandire na je-ka-ka dawo za su ci gaba da karatu – Gwamnatin Katsina

Gwamnatin jihar Katsina ta bai wa makarantun firamare da sakandare na je-ka-ka-dawo damar ci gaba da karatu A wata sanarwa da ma’aikatar ilimi ta jihar ta...

Gwamnatin jihar Bauchi ta rufe dukkanin makarantun da ke fadin jihar

Gwamnatin jihar Bauchi ta sanar da rufe dukkan makarantu firamare, sakandare da manyan makarantu ciki har da na masu zaman kansu sakamakon matsalar tsaro. Rufe makarantun...

Mafi Shahara