DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Jam’iyyar PDP ta bukaci Shugaba Tinubu ya nemi taimako ko ya yi murabus

-

Jam’iyyar PDP ta na shawartar Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya nemi taimako ko ya yi murabus, sakamakon yawaitar hare haren ‘yan bindiga da sace sacen ɗalibai da ya addabi jihohin Arewa a kwanakin nan.

A wani taron manema labarai da jam’iyyar ta yi a Abuja, mai magana da yawunta na ƙasa Ini Ememobong ya ce sace ɗalibai a jihar Kebbi da Niger da kuma masu ibada a Kwara na nuna gazawar Gwamnatin Tinubu wajen magance matsalar tsaro.

Google search engine

A cewar sa gwamnati ta gaza aikinta na kare rayuka da dukiyoyin ‘yan ƙasa, yana mai jaddada cewa idan gwamnati ta kasa wannan aiki to ga dole ta nemi taimako daga cikin gida ko wajen ƙasa.

PDP ta ce matakin rufe wasu makarantun da wasu jihohi ke yi babu inda zai kai, domin hakan kamar mika wuya ne ga ‘yan ta’adda.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara