DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Makarantun Sakandire na je-ka-ka dawo za su ci gaba da karatu – Gwamnatin Katsina

-

Gwamnatin jihar Katsina ta bai wa makarantun firamare da sakandare na je-ka-ka-dawo damar ci gaba da karatu

A wata sanarwa da ma’aikatar ilimi ta jihar ta fitar, ta ce anyi haka ne domin ba da damar zana jarabawar zangon karatu na farko.

Google search engine

Sanarwar ta ce duk da haka dukkannin makarantun kwana za su ci gaba da kasancewa a rufe har sai bayan wani sabon umarni bisa matakan da Gwamnatin jihar Katsina ta dauka don ƙara tsaurara tsaro da kare rayukan ɗalibai da malamai a fadin jihar.

Ma’aikatar ta umurci shugabannin makarantun je-ka-ka dawo da sauran masu ruwa da tsaki su kiyaye tsari da bin dokoki tare da kira ga iyaye su ba ’ya’yansu cikakken goyon baya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gwamnatin jihar Bauchi ta rufe dukkanin makarantun da ke fadin jihar

Gwamnatin jihar Bauchi ta sanar da rufe dukkan makarantu firamare, sakandare da manyan makarantu ciki har da na masu zaman kansu sakamakon matsalar tsaro. Rufe makarantun...

Jam’iyyar PDP ta bukaci Shugaba Tinubu ya nemi taimako ko ya yi murabus

Jam’iyyar PDP ta na shawartar Shugaban Nijeriya Bola Tinubu ya nemi taimako ko ya yi murabus, sakamakon yawaitar hare haren 'yan bindiga da sace sacen...

Mafi Shahara