DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Sace dalibai na barazana ga makomarsu a Arewacin Nijeriya – Amnesty International

-

Kungiyar kare hakkin dan Adam ta Amnesty International a Nigeria ta yi gargadin cewa yawaitar sace dalibai a makarantun arewa na iya karya ilimi, tare da jefa rayuwar yara cikin mummunar makoma.

A wata hirar da ya yi a gidan talabijin na Channels a ranar Litinin, daraktan Amnesty a Nijeriya Isa Sanusi ya ce tsananin tsoro da fargabar sace dalibai na hana su zuwa makaranta, lamarin da ke kara dagula fannin ilimi a yankin.

Google search engine

Sanusi ya bayyana cewa iyayen da ke fama da talauci musamman a karkara na fama wajen tura yaransu makaranta, a yayin da rashin tsaro da sace-sacen yara zai kara hana su yarda da aika ’ya’yansu makaranta.

Ya ce tsoron sace wa kaÉ—ai zai hana dubban yara samun ilimi a arewacin Nijeriya wanda a yanzu yaran da ba sa zuwa makaranta sun haura miliyan 12.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara