DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Harin kwanton-bauna ya yi sanadiyyar ajalin ‘yan sanda hudu a jihar Bauchi

-

An yi wa jami’an ‘yan sanda hudu da aka halaka a kwanakin baya a wani kwanton-bauna a Sabon Sara, Karamar Hukumar Darazo ta Jihar Bauchi, jana’iza a jiya.

Jaridar Daily Trust, ta rawaito cewa jami’an sun fada tarkon ‘yan bindiga ne yayin wani aiki da suke yi a karshen mako.

Google search engine

An gudanar da sallar jana’izar Musulman hudu a Babban Masallacin JIBWIS Gwallaga, tare da rakiyar iyalan mamatan da dubban al’umma zuwa makabartar Dungulbi, inda aka birne su bisa koyarwar addinin Musulunci.

A cikin wata sanarwa, da mai magana da yawun rundunar, SP Ahmed Wakil, ya fitar ya ce rundunar na cikin alhini, yana mai yabawa jarumtar jami’an, ya ce goyon bayan da suka ba al’umma da jajircewar da suka nuna wajen kare rayuka da dukiyoyi ba za a manta wa da shi ba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Za mu fara hukunta duk wani dan kasar waje da wa’adin bizarsa ya kare a Nijeriya kuma ya ci gaba da zama – Gwamnatin...

Gwamnatin Nijeriya ta bayyana cewa yanzu tana da cikakken tsarin gano tare da cafke baƙin ƙasashen waje da suka wuce wa’adin zaman da aka ba...

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

Mafi Shahara