An yi wa jami’an ‘yan sanda hudu da aka halaka a kwanakin baya a wani kwanton-bauna a Sabon Sara, Karamar Hukumar Darazo ta Jihar Bauchi, jana’iza a jiya.
Jaridar Daily Trust, ta rawaito cewa jami’an sun fada tarkon ‘yan bindiga ne yayin wani aiki da suke yi a karshen mako.
An gudanar da sallar jana’izar Musulman hudu a Babban Masallacin JIBWIS Gwallaga, tare da rakiyar iyalan mamatan da dubban al’umma zuwa makabartar Dungulbi, inda aka birne su bisa koyarwar addinin Musulunci.
A cikin wata sanarwa, da mai magana da yawun rundunar, SP Ahmed Wakil, ya fitar ya ce rundunar na cikin alhini, yana mai yabawa jarumtar jami’an, ya ce goyon bayan da suka ba al’umma da jajircewar da suka nuna wajen kare rayuka da dukiyoyi ba za a manta wa da shi ba.



