Gwamnonin yankin Kudu Maso Yamma sun sake jaddada bukatar kafa ‘yan sandan jihohi, suna cewa karuwar matsalolin tsaro a fadin Nijeriya ta kai matakin da ba za a yi gum ba.
Gwamnonin sun bayyyana haka ne bayan taron gaggawa da suka gudanar a Ibadan, jihar Oyo.
A cikin wata sanarwa da suka fitar, Gwammnonin karkashin jagorancin gwamnan Legasa Babajide Sanwo-Olu, dukkanninsu sun amince da matsayar da aka cimma.
A cewar sanarwar, gwamnonin sun bukaci Gwamnatin tarayya ta gaggauta shiga cikin batun tsare-tsaren dazuzzuka, wadanda suka ce sun zama maboyar miyagu, yayin da suka tabbatar da bukatar kafa ‘yan sandan jihohi abinda suka ce sune za su daukin nauyinsu, saboda za su taimaka wajen dakile matsalar tsaro da ake fama da ita.



