Madugun adawa a Nijeriya Atiku Abubakar, ya soki gwamnatin tarayya kan hanyar da aka bi wajen sakin ‘yan matan da aka sace a Kebbi, yana mai cewa bai kamata a nuna shi a matsayin nasara ba, illa hakan na nuna tabarbarewar lamarin tsaron kasar.
A wata sanarwa da ofishin yada labaran Atiku ya fitar a ranar Laraba, ya ce babban abin damuwa shi ne yadda ‘yan ta’adda a halin yanzu ke yawo babu tsoro, suna tattaunawa, suna kuma sa dokoki da suke so a bi.
A wata sanarwa da mai bai wa shugaban Tinubu shawara kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga ya fitar, ya bayyana cewa DSS da sojoji sun bibiyi ‘yan bindigar kai tsaye a lokacin harin, har suka samu damar tattaunawa da su don a sako daliban ba tare da biyan kudin fansa ba.
Sai dai Atiku ya bayyana wannan magana a matsayin kokarin rufe bakin jama’a da kuma juya gazawar gwamnati ta koma nasara.



