DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Bai kamata a nuna sakin yaran da aka sace a matsayin nasara ga gwamnati ba – Atiku Abubakar

-

Madugun adawa a Nijeriya Atiku Abubakar, ya soki gwamnatin tarayya kan hanyar da aka bi wajen sakin ‘yan matan da aka sace a Kebbi, yana mai cewa bai kamata a nuna shi a matsayin nasara ba, illa hakan na nuna tabarbarewar lamarin tsaron kasar.

A wata sanarwa da ofishin yada labaran Atiku ya fitar a ranar Laraba, ya ce babban abin damuwa shi ne yadda ‘yan ta’adda a halin yanzu ke yawo babu tsoro, suna tattaunawa, suna kuma sa dokoki da suke so a bi.

Google search engine

A wata sanarwa da mai bai wa shugaban Tinubu shawara kan harkokin yada labarai Bayo Onanuga ya fitar, ya bayyana cewa DSS da sojoji sun bibiyi ‘yan bindigar kai tsaye a lokacin harin, har suka samu damar tattaunawa da su don a sako daliban ba tare da biyan kudin fansa ba.

Sai dai Atiku ya bayyana wannan magana a matsayin kokarin rufe bakin jama’a da kuma juya gazawar gwamnati ta koma nasara.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara