DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Ƴan Nijeriya na da ƴancin neman taimakon ƙasashen waje kan matsalar tsaro idan gwamnati ta kasa – Obasanjo

-

Tsohon shugaban Nijeriya Olusegun Obasanjo ya ce ’yan Nijeriya na da cikakken ’yancin neman taimakon kasashen waje idan gwamnatin Nijeriya ta gaza kare rayukansu.

Obasanjo ya yi jawabin ne yayin wani taron Kirsimeti a Jos, inda ya ce bai kamata a ji kunyar neman taimako ba idan gwamnati ta kasa cika babban nauyinta na tsaro.

Google search engine

channels TV ta ruwaito Obasanjo ya ce a zamanin da ake amfani da tauraron dan adam da jiragen sintiri, bai kamata ’yan ta’adda su rika kashe mutane su bace ba. Ya zargi gwamnati da gazawa, yana mai cewa hare-hare da kashe-kashe sun yi yawa, kuma ’yan kasa sun gaji da zubar da jini.

Hakazalika, ya tuna da sace ’yan matan Chibok, yana mai cewa matsalar tsaro ta kara tabarbarewa maimakon ta inganta, kuma ya jaddada cewa kariyar ’yan kasa ita ce aikin farko na kowace gwamnati, amma a halin yanzu gwamnati ba ta iya kare al’umma yadda ya kamata ba.

Obasanjo ya kuma yi Allah-wadai da masu kokarin mayar da kashe-kashe batun addini ko kabila, yana mai cewa “dukkanmu ’yan Nijeriya ne, kuma ana kashe mu ba tare da bambanci ba.”

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Majalisar wakilan Nijeriya za ta yi zaman gaggawa kan jadawalin zaben 2027

Majalisar Wakilan Nijeriya za ta koma zama ranar Talata, 17 ga Fabrairu, domin tattauna batutuwan zabe da suka taso bayan sanar da jadawalin zaben 2027...

Kotu ta sahale a binciko takardun karatun Ministan cikin gida na Nijeriya Olubunmi Tunji-Ojo

Babbar Kotun Tarayya da ke Abuja ta amince da bukatar binciken ingancin takardar shaidar sakandare ta Ministan Harkokin Cikin Gida, Olubunmi Tunji-Ojo. Mai shari’a Binta Nyako...

Mafi Shahara