DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Juyin mulkin Guinea Bissau ya fi mini ciwo fiye da shan kaye a zaben 2015 – Jonathan

-

Tsohon Shugaban Nijeriya, Goodluck Jonathan ya bayyana cewa juyin mulkin da ya faru a Guinea Bissau ya fi masa ciwo fiye da lokacin da ya kira Muhammadu Buhari ya taya shi murna a zaben 2015 da ya sha kaye.

A cewarsa, lamarin ya taba shi sosai domin ya dade yana taka rawa wajen dawo da dimokuradiyya a kasar kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

Google search engine

A lokacin rikicin, Jonathan ya je Guinea Bissau ne a matsayin wakilin kungiyar dattawan Yammacin Afrika don sa ido kan zaben kasar, tare da tawagogin AU da ECOWAS. Sai dai kafin su kammala aikinsu, rundunar soji ta kwace mulki, lamarin da ya bar shi da tawagarsa cikin fargaba har aka kwashe su aka dawo da su Nijeriya ranar Alhamis.

Jonathan ya ce abin ya daga masa hankali sosai saboda bai taba tunanin zai tsinci kansa a irin wannan yanayi ba.

Hakazalika ya kara da cewa, abin da ya faru a Guinea Bissau ya fi masa ciwo fiye da ranar da ya kira Buhari bayan ya sha kaye a zabe, domin shi mutum ne da yake da yakinin dimokuradiyya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Shehu Sani ya karyata El-Rufai kan batun bacewar Dadiyata

Tsohon Sanatan Kaduna ta Tsakiya, Comrade Shehu Sani, ya karyata ikirarin tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, cewa Abubakar Idris wanda aka fi sani da...

Majalisar wakilan Nijeriya za ta yi zaman gaggawa kan jadawalin zaben 2027

Majalisar Wakilan Nijeriya za ta koma zama ranar Talata, 17 ga Fabrairu, domin tattauna batutuwan zabe da suka taso bayan sanar da jadawalin zaben 2027...

Mafi Shahara