DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Shugaba Tinubu ya sake miƙa sunayen sabbin Jakadu 32 ga majalisa domin tabbatarwa

-

Shugaba Bola Ahmed Tinubu ya sake aika sunayen mutane 32 ga Majalisar Dattawa don tantancewa a matsayin sabbin jakadu, kwanaki kaɗan bayan turo rukuni na farko na mutane uku.

A cewar wasikun da ya aika wa Shugaban Majalisar Dattawa, Sanata Godswill Akpabio, an nemi a gaggauta tantance jakadu 32, inda mata goma ke cikin jerin sunayen.

Google search engine

Daga cikin sunayen sun haɗa da Barr. Ogbonnaya Kalu, Reno Omokri, tsohon shugaban INEC Prof. Mahmud Yakubu, Erelu Angela Adebayo, da tsohon gwamnan Enugu Ifeanyi Ugwuanyi, tare da wasu shugabanni daga jihohi daban-daban ciki har da Tasiu Maigari, Prof. Nora Daduut, Femi Pedro, Femi Fani-Kayode, Fatima Ajimobi, Lola Akande da Victor Ikpeazu.

Hakazalika akwai Enebechi Okwuchukwu (Abia), Yakubu Danladi (Taraba), Miamuna Besto (Adamawa), Musa Abubakar (Kebbi), Syndoph Endoni (Bayelsa), Chima David (Ebonyi), Mopelola Adeola-Ibrahim (Ogun), da wasu jakadu daga jihohi daban-daban.

Ana sa ran za a tura sabbin jakadun zuwa ƙasashe masu muhimmancin hulɗa da Nijeriya kamar China, India, Canada, Mexico, UAE, Qatar, South Africa da Kenya, da cibiyoyi irin su Majalisar Dinkin Duniya, UNESCO da Tarayyar Afirka, bayan tantancewarsu.

A makon da ya wuce Tinubu ya aika sunayen mutum uku na farko don a tura su zuwa UK, Amurka ko Faransa, inda ya tabbatar da cewa za a fitar da ƙarin sunayen jakadu nan gaba.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara