Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya yaba wa majalisar dattawa kan saurin tabbatar da Janar Christopher Musa (ritaya) a matsayin sabon ministan tsaro, yana mai cewa nadin ya zo a lokacin da kasa ke fuskantar manyan kalubale.
A cikin sakon da ya wallafa a shafinsa na X a ranar Alhamis, Tinubu ya ce ya mika sunan Musa ga majalisar kwanaki biyu da suka gabata domin tantancewa da tabbatarwa.
Ya bayyana tsohon CDS din a matsayin “mutumin kirki” da ƙwarewarsa za ta taka muhimmiyar rawa wajen magance matsalolin tsaro.




