Gwamnatin Nijeriya ta sha alwashin kammala biyan bashin da ‘yan kwangila ke bin ta, daga yanzu zuwa ranar 20 ga watan Disamban 2025.
Wannan dai na a matsayin wani yunkuri na daidaita lamura, biyo bayan zanga-zangar da ‘yan kwangilar suka fara gudanarwa kan halin da suke ciki.
Jaridar Punch ta ruwaito cewa ministan ayyuka na Nijeriya David Umahi ne ya bayar da tabbacin a jihar Nassarawa, inda ya ce shugaba Tinubu ya amince da kafa wani kwamiti da zai bibiya tare da tabbatar da cewa an biya su hakkokinsu.



