DCL Hausa Radio
Kaitsaye

An kaddamar da kafar yaɗa labarai ta Hausa don mata zalla a Nijeriya

-

An kaddamar da Mata Media, kafar yaɗa labarai ta farko a Nijeriya da aka ware musamman domin mata, wacce ke aikin shirya labarai na abubuwan da suka shafi mata, ta hannun mata, domin mata.

Ƙwararrun mata ‘yan jarida da suka goge kuma waɗanda suka jajirce wajen tallafa wa mata, su ne suka kafa “Mata Media“ domin samar da kafar da za ta riƙa tattaunawar da ta shafi rayuwar mata.

Google search engine

Da take jawabi a yayin ƙaddamarwar, Fauziyya Kabir Tukur, babbar manajar kafar yada labaran Mata Media, ta ce an fito da wannan kafar ne don cike giɓin da ya dade a bangaren yaɗa labarai na Hausa.

“MUNA ALFAHARI DA KADDAMAR DA MATA MEDIA, SABUWAR KAFA MAI KISHIN MATA. BURINMU SHI NE SAMAR DA DANDALIN DA MATA ZA SU JI DAƊIN BA DA LABARANSU, BAYYANA RA’AYOYINSU DA DAMUWARSU CIKIN ‘YANCI, TARE DA KARFAFA  MATAN SHIGA HARKOKIN SHUGABANCI,” IN JI TA.

Daga cikin muhimman manufofin Mata Media akwai daukar nauyin horas da matasan mata ‘yan jarida, ta hanyar bayar da dama ga masu koyon aiki da sabbin shigowa su samu kwarewa a aikin jarida na Hausa.

Fauziyya wadda tsohuwar ma’aikaciyar BBC ce ta ce a halin yanzu, Mata Media na aiki ne kacokan ta yanar gizo, da shafukan sada zumunta na Facebook, Instagram, TikTok, YouTube.

A ƙarshe, babbar manajar ta yi kira ga sauran kafafen yaɗa labarai da masu ruwa da tsaki su yi aiki tare da Mata Media domin ƙara ɗaga murya da tasirin mata a Nijeriya.

Ukashatu Ibrahim Wakili
Ukashatu Ibrahim Wakilihttp://dclhausa.com
Ukashatu Wakili, Mataimakin Babban Edita kuma Mai Kula da Shirin Koyon Sanin Makamar Aiki ne a DCL Hausa. A matsayinsa na ƙwararren ɗan jarida yana tsara ayyukan rediyo da kafafen sada zumunta, fassarar labarai, da tabbatar da sahihancin bayanai. Yana jagorantar shirin horaswa ga masu koyon aiki tare da kula da ingancin rubuce-rubuce da shirye-shiryen gidan jaridar.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Ku daina nada baragurbin ‘yan siyasa a shugabacin Jami’o’i – Jega ga Tinubu

Tsohon shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC, Farfesa Attahiru Jega, ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta daina nada ’yan siyasa marasa kwarewa da mutanen...

NSA Ribadu ya gana da tawagar Majalisar Dokokin Amurka a Abuja

Mai ba shugaban Nijeriya shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, ya karɓi wata tawagar ‘yan majalisar dokokin Amurka a Abuja, domin ci gaba da tattaunawa kan...

Mafi Shahara