DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Faransa ta sha alwashin tallafa wa Nijeriya a yaki da ’yan ta’adda

-

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bayyana cikakken goyon bayan kasarsa ga Najeriya wajen yaki da matsalar tsaro, musamman barazanar ta’addanci da ake fuskanta a Arewa.

A wani saƙo da ya wallafa a X a ranar Lahadi, Macron ya ce ya yi magana da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, inda ya tabbatar masa cewa Faransa za ta ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da gwamnatin Najeriya.

Google search engine

Sanarwar ta Macron na zuwa ne bayan ƙarin hare-hare da garkuwa da mutane a yankin Arewa, lamarin da ya ja hankalin ƙasashen duniya.

Najeriya na ci gaba da neman goyon bayan ƙasashen duniya, ciki har da tattaunawar da Mai bai wa Shugaban kasa shawara kan tsaro, Mallam Nuhu Ribadu, ya yi da Sakataren harkokin Yaƙin Amurka, Pete Hegseth, a Pentagon domin inganta dabarun yaki da ta’addanci a Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

An kaddamar da kafar yaɗa labarai ta Hausa don mata zalla a Nijeriya

An kaddamar da Mata Media, kafar yaɗa labarai ta farko a Nijeriya da aka ware musamman domin mata, wacce ke aikin shirya labarai na abubuwan...

Ku daina nada baragurbin ‘yan siyasa a shugabacin Jami’o’i – Jega ga Tinubu

Tsohon shugaban hukumar zaben Nijeriya INEC, Farfesa Attahiru Jega, ya yi kira ga Gwamnatin Tarayya da ta daina nada ’yan siyasa marasa kwarewa da mutanen...

Mafi Shahara