DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Faransa ta sha alwashin tallafa wa Nijeriya a yaki da ’yan ta’adda

-

Shugaban Faransa Emmanuel Macron ya bayyana cikakken goyon bayan kasarsa ga Najeriya wajen yaki da matsalar tsaro, musamman barazanar ta’addanci da ake fuskanta a Arewa.

A wani saƙo da ya wallafa a X a ranar Lahadi, Macron ya ce ya yi magana da Shugaba Bola Ahmed Tinubu, inda ya tabbatar masa cewa Faransa za ta ƙara ƙarfafa haɗin gwiwa da gwamnatin Najeriya.

Google search engine

Sanarwar ta Macron na zuwa ne bayan ƙarin hare-hare da garkuwa da mutane a yankin Arewa, lamarin da ya ja hankalin ƙasashen duniya.

Najeriya na ci gaba da neman goyon bayan ƙasashen duniya, ciki har da tattaunawar da Mai bai wa Shugaban kasa shawara kan tsaro, Mallam Nuhu Ribadu, ya yi da Sakataren harkokin Yaƙin Amurka, Pete Hegseth, a Pentagon domin inganta dabarun yaki da ta’addanci a Nijeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Kotun kolin Nijeriya ta yi watsi da karar da ake zargin Manjo Al Mustapha da hannu wajen halaka matar Abiola

Kotun Kolin Nijeriya ta yi watsi da shari’ar da aka shigar da Manjo Hamza Al Mustapha, kan zarginsa da hannu wajen halaka Kudirat Abiola, matar...

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea Bissau sun saka ƙarshen shekarar 2026 don gudanar da zaɓe a ƙasar

Sojojin da suka yi juyin mulki a Guinea-Bissau sun ce za a gudanar shugaban ƙasa a ranar 6 ga Disambar 2026, bayan da suka kifar...

Mafi Shahara