ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a ƙasashen yammacin Afirka saboda ƙaruwar juyin Mulki
Kungiyar ECOWAS ta ayyana dokar gaggawa a duk fadin Yammacin Afrika, sakamakon tabarbarewar tsaro da karuwar kalubalen siyasa a kasashen mambobi.
Shugaban Hukumar ECOWAS, Omar Touray, ne ya sanar da hakan a Abuja yayin zaman Majalisar Sulhu da Zaman Lafiya ta ministoci.
Touray ya ce rahotannin da ke gaban ministocin sun nuna cewa mafi yawan kasashen yankin suna cikin matakin haɗari mai tsanani, daga juyin mulki, wahalar sauyin mulki, takura wa zabe, karuwar ayyukan ta’addanci, zuwa matsin lambar ƙasashen waje kan dangantaka da manufofin yankin.
Ya ce abubuwan da suka faru kwanakin nan ciki har da yunkurin juyin mulki a Guinea-Bissau da Jamhuriyar Benin sun tabbatar da bukatar daukar matakin gaggawa.
Ya jaddada cewa zabe ya zama babban abin tayar da hankalin siyasa a yankin, tare da ci gaba da barazanar ‘yan ta’adda, da kuma masu tayar da tarzoma a iyakoki.



