DCL Hausa Radio
Kaitsaye

ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a ƙasashen yammacin Afirka

-

ECOWAS ta ayyana dokar ta-baci a ƙasashen yammacin Afirka saboda ƙaruwar juyin Mulki

Kungiyar ECOWAS ta ayyana dokar gaggawa a duk fadin Yammacin Afrika, sakamakon tabarbarewar tsaro da karuwar kalubalen siyasa a kasashen mambobi.

Google search engine

Shugaban Hukumar ECOWAS, Omar Touray, ne ya sanar da hakan a Abuja yayin zaman Majalisar Sulhu da Zaman Lafiya ta ministoci.

Touray ya ce rahotannin da ke gaban ministocin sun nuna cewa mafi yawan kasashen yankin suna cikin matakin haɗari mai tsanani, daga juyin mulki, wahalar sauyin mulki, takura wa zabe, karuwar ayyukan ta’addanci, zuwa matsin lambar ƙasashen waje kan dangantaka da manufofin yankin.

Ya ce abubuwan da suka faru kwanakin nan ciki har da yunkurin juyin mulki a Guinea-Bissau da Jamhuriyar Benin sun tabbatar da bukatar daukar matakin gaggawa.

Ya jaddada cewa zabe ya zama babban abin tayar da hankalin siyasa a yankin, tare da ci gaba da barazanar ‘yan ta’adda, da kuma masu tayar da tarzoma a iyakoki.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara