DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Nijeriya ta tura manyan aiyukanta na 2025 zuwa kasafin 2026

-

Gwamnatin Nijeriya ta dage aiwatar da kashi 70% na manyan ayyukan 2025 zuwa 2026 saboda karancin kudaden shiga da kuma bukatar kammala ayyukan da ake kan yi.

Cikin wani rahoto da jaridar Punch ta fitar, sabon umarnin ma’aikatar tsare-tsaren tattalin arziki ya hana sabbin manyan ayyuka a kasafin 2026, inda ma’aikatun gwamnati za su ci gaba da aiki da kudaden da aka ware musu a 2025.

Google search engine

Sanarwar tace kashi 30% na kasafin manyan ayyuka na bana ne kawai za a saki, sauran 70% za su zama tushen kasafin 2026, an kuma umurci hukumomin da kada su wuce iyakar kashe kudin ‘overhead’ na shekarar da ta gabata.

Gwamnati ta ce hakan zai inganta tsari, rage batar da kudi, kuma ya tabbatar da cewa kudin gwamnati ya tafi kan muhimman abubuwa kamar tsaro, tattalin arziki, ilimi, lafiya da makamashi.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara