Gwamnatin Nijeriya ta dage aiwatar da kashi 70% na manyan ayyukan 2025 zuwa 2026 saboda karancin kudaden shiga da kuma bukatar kammala ayyukan da ake kan yi.
Cikin wani rahoto da jaridar Punch ta fitar, sabon umarnin ma’aikatar tsare-tsaren tattalin arziki ya hana sabbin manyan ayyuka a kasafin 2026, inda ma’aikatun gwamnati za su ci gaba da aiki da kudaden da aka ware musu a 2025.
Sanarwar tace kashi 30% na kasafin manyan ayyuka na bana ne kawai za a saki, sauran 70% za su zama tushen kasafin 2026, an kuma umurci hukumomin da kada su wuce iyakar kashe kudin ‘overhead’ na shekarar da ta gabata.
Gwamnati ta ce hakan zai inganta tsari, rage batar da kudi, kuma ya tabbatar da cewa kudin gwamnati ya tafi kan muhimman abubuwa kamar tsaro, tattalin arziki, ilimi, lafiya da makamashi.



