DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Tinubu ya taimaki Nijeriya ta hanyar dakile juyin mulkin Benin

-

Kungiyar Gwamnonin Najeriya ta bayyana cewa gaggawar daukar matakin Shugaba Bola Ahmed Tinubu wajen dakile yunkurin juyin mulki a Jamhuriyar Benin ta hana afkuwar babbar barazanar tsaro ga Najeriya.

Shugaban kungiyar kuma Gwamnan Jihar Kwara, AbdulRahman AbdulRazaq, ya ce idan juyin mulkin ya yi nasara, zai ba wa ‘yan bindiga da sauran kungiyoyin da ke aiki a yankin Sahel damar kara tayar da hankula a Najeriya, musamman ganin cewa wasu sassan Benin sun riga sun cika da gungun masu bore.

Google search engine

Jaridar Punch ta ambato shi na cewa rushewar tsarin mulki a Benin zai iya shafar yankunan kan iyaka na Najeriya kai tsaye.

Gwamnonin sun jinjinawa Sojojin Najeriya bisa saurin mayar da martani da ya taimaka wajen dawo da daidaito a Benin, tare da jaddada cewa barazanar tsaro ga manyan biranen Benin kamar Porto Novo, Cotonou ko Parakou na da tasiri kai tsaye ga Najeriya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara