Farfesa Wole Soyinka ya gargadi Shugaba Bola Tinubu da ya kula da yadda ake amfani da jami’an tsaro ga wasu mutane na musamman, musamman dangin masu mulki.
Rahoton Jaridar Punch ya ce ya ce Soyinka ya ga abin mamaki a wani otel a Ikoyi, yayin da ake bai wa Seyi Tinubu, ɗan shugaban ƙasa tsatstsauran tsaro da yace sun isa kwace karamar kasa.
Soyinka ya ce abin ya dame shi sosai, har ya kira mai ba shugaban ƙasa shawara kan tsaro, Nuhu Ribadu, domin jin dalili.
Kodayake ya yi jawabin ne cikin barkwanci cewa, idan rikici ya tashi a ƙasa, “ko a tura Seyi ya je ya magance shi tunda yawan tsaron nasa ya yi yawa,” amma ya nuna cewa akwai bakatar adalci a tsaron al’umma.



