Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu ya sake jaddada cewa babu wani kisan kare dangi da ake yi a kan mabiya wani addini a kasar, walau Musulmi ko mabiya addinin Kirista.
Tinubu ta bakin babban lauyan gwamnati kuma ministan shari’a Lateef Fagbemi SAN, ya bayyana haka ne a Abuja, a wajen taron kungiyar Nasrul-Lahi-l-Fatih karo na 8, kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.
A cewar sa, hare-haren da ake samu sun samo asali ne daga tarihi, matsalolin tattalin arziki da kuma wanzuwar ayyukan ta’addanci, yana mai cewa basu da alaka da wani addini.



