DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin jihar Bayelsa ta umurci binciken gawar mataimakin gwamnnan domin gano musabbabin mutuwar fuju’arsa

-

Gwamnan Jihar Bayelsa, Sanata Douye Diri, ya bayar da umarnin a gudanar da bincike (autopsy) kan gawar marigayi mataimakinsa, Sanata Lawrence Ewhrudjakpo, domin gano ainihin musabbabin mutuwarsa.

Gwamna Diri ya bayyana hakan ne a ranar Asabar yayin da tsohon Shugaban Nijeriya, Dr Goodluck Jonathan, ya kai masa ziyarar ta’aziyya a fadar gwamnati da ke Yenagoa.

Google search engine

Diri ya ce umarnin ya zama dole ne sakamakon jita-jita da ke yawo a kafafen sada zumunta game da mutuwar mataimakin gwamnan kamar yadda jaridar Punch ta ruwaito.

A nasa bangaren, Jonathan ya bayyana mutuwar Ewhrudjakpo a matsayin babban rashi ga al’ummar Bayelsa, yana mai cewa marigayin ya kasance mutum mai himma da aminci, wanda ya wakilci gwamnan jihar a shirye-shiryen Gidauniyar Jonathan, ciki har da taron Democracy Dialogue da aka gudanar a Benin, Jihar Edo.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Mun saurari kiran da aka ba da umarnin kama ni bayan wani ya yi kutsen wayar Ribadu – El-Rufai

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya ce ya saurari wata tattaunawar waya da ya danganta da Mai Ba Shugaban Ƙasa Shawara kan Tsaro (NSA),...

El-Rufai ya zargi gwamnatin Tinubu da hannu a yunƙurin sanya Kwankwaso cikin jerin takunkumin Amurka

Tsohon gwamnan Kaduna, Malam Nasir El-Rufai, ya yi zargin cewa gwamnatin Shugaba Bola Ahmed Tinubu na iya kasancewa a bayan yunƙurin dan Majalisar Dokokin Amurka,...

Mafi Shahara