Manyan jagororin adawa sun zargi gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da amfani da EFCC da sauran hukumomi wajen tsoratar da ‘yan adawa da raunana tsarin jam’iyyu da dama a Najeriya.
Sun ce ana fifita wasu wajen aiwatar da doka, inda ake matsa wa ‘yan adawa lamba yayin da ake watsi da zarge-zarge kan ‘yan jam’iyya mai mulki.
Jagororin sun bukaci a kare ‘yancin EFCC, a kafa hukumar bincike mai zaman kanta da za ta duba asusun gwamnati daga 2015 zuwa 2025, tare da saka matakan rigakafin cin hanci kai tsaye cikin harkokin biyan kudi na gwamnati.
Sun yi gargadin cewa idan ba a dakatar da wannan salo ba, dimokuradiyyar Najeriya na fuskantar barazana gabanin zaben 2027.
Saidai fadar shugaban kasa ta sha musanta wannan zargin.



