DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Dimokuradiyyar Najeriya na cikin hadari gabanin zaben 2027 – shugabannin adawa

-

Manyan jagororin adawa sun zargi gwamnatin Shugaba Bola Tinubu da amfani da EFCC da sauran hukumomi wajen tsoratar da ‘yan adawa da raunana tsarin jam’iyyu da dama a Najeriya.

Sun ce ana fifita wasu wajen aiwatar da doka, inda ake matsa wa ‘yan adawa lamba yayin da ake watsi da zarge-zarge kan ‘yan jam’iyya mai mulki.

Google search engine

Jagororin sun bukaci a kare ‘yancin EFCC, a kafa hukumar bincike mai zaman kanta da za ta duba asusun gwamnati daga 2015 zuwa 2025, tare da saka matakan rigakafin cin hanci kai tsaye cikin harkokin biyan kudi na gwamnati.

Sun yi gargadin cewa idan ba a dakatar da wannan salo ba, dimokuradiyyar Najeriya na fuskantar barazana gabanin zaben 2027.

Saidai fadar shugaban kasa ta sha musanta wannan zargin.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Dan majalisar wakilan Nijeriya ya sauys sheka daga PDP zuwa ADC

Dan majalisar tarayya mai wakiltar mazabar Tambuwal/Kebbe a jihar Sokoto, Abdussamad Dasuki ya sanar da ficewarsa daga jam’iyyar PDP, inda ya koma ADC. A cikin wasiƙar...

Sanata Wamako ya raba wa marayu su 10,000 tallafin N1,000 kowane a jihar Sokoto

Tsohon gwamnan jihar Sokoto kuma Sanata mai wakiltar Sokoto ta Arewa, Aliyu Magatakarda Wamakko, ya bayar da tallafin miliyan 10, ga mutane dubu 10 da...

Mafi Shahara