DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan sandan Nijeriya sun sanar da dawo da aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu

-

Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya ta sanar da cewa za ta sake fara aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu (Tinted Glass Permit), duk da cewa har yanzu batun yana gaban kotu. Rundunar ta bayyana cewa babu wani umarnin kotu da ya hana ta aiwatar da dokar, sai dai a baya ta dakatar da hukunta masu laifi ne domin bai wa masu mota damar daidaita takardunsu cikin sauki. Sai dai yanzu, ‘yan sanda sun ce karuwar laifuka da ake aikatawa ta amfani da motoci masu gilashi masu duhu ba tare da izini ba ya tilasta musu daukar mataki cikin gaggawa.

A cewar Rundunar, wasu bata-gari da kungiyoyin masu aikata manyan laifuka na amfani da irin wadannan motoci wajen boye fuskokinsu domin aikata fashi da makami, garkuwa da mutane da sauran laifuka masu tsanani. Saboda haka, rundunar ta sanar da cewa aiwatar da dokar lasisin gilashin mota mai duhu zai fara ne daga 2 ga watan Janairu, 2026. Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, IGP Kayode Adeolu Egbetokun, ya tabbatar wa ‘yan kasa cewa za a aiwatar da dokar cikin kwarewa, mutunta hakkin jama’a, da bin doka da oda, tare da kira ga masu motoci da su nemi lasisin ta hanyoyin da aka amince da su.

Google search engine

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Idan rikicin PDP ya ki ci, ya ki cinyewa za mu shiga kawance in ji Sule Lamido

Tsohon Gwamnan Jihar Jigawa, Alhaji Sule Lamido, ya bayyana cewa dole na iya sanyawa jam’iyyar ta shiga kawance da wasu jam’iyyu idan ƙoƙarin da ake...

Nijeriya ta musanta zargin leken asiri kan jirginta da ke Burkina-Faso

Rundunar Sojin Sama ta Najeriya ta musanta zargin leken asiri da ake jinginawa jirginta a Burkina-Faso Rundunar Sojin Sama ta Najeriya (NAF) ta karyata jita-jitar da...

Mafi Shahara