DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Kotu ta amince ta bai wa Ngige beli tare da sharaɗin nemo babban jami’in gwamnati da zai tsaya masa

-

Babbar Kotun Abuja da ke Gwarinpa, ta amince tsohon Ministan Kwadago, Chris Ngige, ya cigaba da cin gajiyar belin da hukumar EFCC ta ba shi tun da farko.

Alkaliyar kotun, Mai shari’a Maryam Hassan, ta bayar da wannan hukunci ne yayin yanke shawara kan bukatar beli da lauyan Ngige, Barista Patrick Ikwueto (SAN), ya shigar a madadinsa.

Google search engine

Kotun ta umarci Ngige da ya gabatar da mai tsaya masa wanda dole ne ya kasance darakta a aikin Gwamnatin Tarayya kuma mai fili. Haka kuma, kotun ta ce dole ne mai tsayawar ya ajiye takardun filin da kuma takardun tafiyarsa a gaban kotu har sai Ngige ya karbo fasfonsa na kasa da kasa.

Tun da farko, EFCC ta ba Ngige beli ne bisa amincewar kansa, inda ta umarce shi da ya mika takardun tafiyarsa tare da gabatar da mai tsaya masa guda daya.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Obasanjo ya nuna jarumtaka da sadaukarwa wajen yi wa Nijeriya hidima – Shugaba Tinubu

Shugaban Nijeriya Bola Ahmed Tinubu, ya taya tsohon shugaban ƙasar Olusegun Obasanjo murnar cika shekaru 89 da haihuwa. A cikin wata sanarwa da mai magana da...

China ta umurci matatun man fetur din ta su dakatar da jigilar sa saboda rikicin Gabas ta tsakiya

Gwamnatin China ta umurci manyan matatun man fetur na ƙasar da su dakatar da fitar da dizal da fetur zuwa ƙasashen waje na ɗan lokaci,...

Mafi Shahara