DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gasar cin kofin kasashen nahiyar Afirka AFCON za ta koma duk bayan shekaru 4 – CAF

-

Hukumar kwallon kafa ta nahiyar Afrika CAF, ta sanar da cewa gasar cin kofin kasashen Afrika AFCON, za ta koma duk bayan shekara huɗu bayan kammala gasar da aka tsara a 2028.

Shugaban na CAF, Patrice Motsepe, ne ya bayyana hakan a ranar Asabar yayin ganawa da manema labarai a Rabat, da ke Maroko, inda ya ce sauyin yana cikin gyaran tsarin wasannin ƙwallon ƙafa a nahiyar domin ya dace da jadawalin wasannin duniya.

Google search engine

Motsepe ya bayyana cewa duk da AFCON na taimaka wa ƙungiyoyin ƙasashe ta fuskar kuɗaɗe, CAF ta yanke shawarar ƙaddamar da gasar African Nations League wadda za a rika yi kowace shekara, makamanciyar UEFA Nations League.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Tinubu ya ziyarci jihar Borno domin bude ayyuka

Shugaba Tinubu, ya ziyarci Maiduguri, babban birnin Jihar Borno, domin ƙaddamar da manyan ayyuka da halartar bikin auren ɗan tsohon gwamnan jihar, Sanata Ali Modu...

‘Yan bindiga za su dandana kudarsu a shekarar 2026 – Kwamandan sojin Nijeriya, Birgediya Janar Adebisi Onasan

Kwamandan rundunar sojin Nijeriya ta Guwards Brigade , Birgediya Janar Adebisi Onasanya, ya gargaɗi ’yan bindiga da sauran masu aikata laifuka a Abuja da sauran...

Mafi Shahara