DCL Hausa Radio
Kaitsaye

‘Yan bindiga za su dandana kudarsu a shekarar 2026 – Kwamandan sojin Nijeriya, Birgediya Janar Adebisi Onasan

-

Kwamandan rundunar sojin Nijeriya ta Guwards Brigade , Birgediya Janar Adebisi Onasanya, ya gargaɗi ’yan bindiga da sauran masu aikata laifuka a Abuja da sauran wurare cewa za su dandana kudarsu a shekarar 2026, domin za a ƙara matsa musu lamba ta fuskar tsaro.

Janar Onasanya ya bayyana hakan ne a Abuja a ranar Asabar, yayin ganawa da manema labarai a Aso Rock.

Google search engine

Ya bayyana cewa shekarar 2025 ta kasance mai matuƙar ƙalubale, sakamakon ƙarin buƙatun tsaurara tsaro fiye da aikin kare shugabanni kaɗai.

A cewarsa, rundunar ta tsabtace yankuna a wurare daban daban a Abuja da wasu sassan jihar Neja, inda aka kama masu laifi, aka kwato makamai, tare wasu ’yan ta’adda,ya ce nasarorin sun samu ne ta hanyar haɗin gwiwa da ’yan sanda, NSCDC, DSS, da kuma goyon bayan sojin ruwa da sojin sama.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Gasar cin kofin kasashen nahiyar Afirka AFCON za ta koma duk bayan shekaru 4 – CAF

Hukumar kwallon kafa ta nahiyar Afrika CAF, ta sanar da cewa gasar cin kofin kasashen Afrika AFCON, za ta koma duk bayan shekara huɗu bayan...

Tinubu ya ziyarci jihar Borno domin bude ayyuka

Shugaba Tinubu, ya ziyarci Maiduguri, babban birnin Jihar Borno, domin ƙaddamar da manyan ayyuka da halartar bikin auren ɗan tsohon gwamnan jihar, Sanata Ali Modu...

Mafi Shahara