DCL Hausa Radio
Kaitsaye

Gwamnatin Nijeriya ta ayyana Alhamis da Juma’a a matsayin ranakun hutun Kirsimeti da Boxing Day

-

Gwamnatin Nijeriya ta ayyana Alhamis 25 ga Disamba da Juma’a 26 ga Disamba, 2025 a matsayin ranakun hutun Kirsimeti da Boxing Day, tare da ayyana Alhamis 1 ga Janairu, 2026 domin bikin Sabuwar Shekara.

Sanarwar ta fito ne cikin wata sanarwa da Babbar Sakatariyar Ma’aikatar Harkokin Ciki, Dakta Magdalene Ajani, ta fitar a madadin Ministan Harkokin Ciki, Olubunmi Tunji-Ojo, a ranar Litinin.

Google search engine

Ministan ya buƙaci ’yan Nijeriya su yi amfani da lokacin bukukuwan wajen tunani kan ƙauna, zaman lafiya da sadaukarwa, tare da yin addu’o’i domin zaman lafiya, ingantaccen tsaro da ci gaban ƙasa, yana kuma yi wa al’umma fatan barka da Kirsimeti da sabuwar shekara mai albarka.

LEAVE A REPLY

Please enter your comment!
Please enter your name here

Sabbin Labarai

Har yanzu bamu kammala bincike ba shiyasa bamu gurfanar da El-rufa’i a gaban kotu ba – EFCC

Hukumar EFCC, mai yaki a cin hanci da rashawa a Nijeriya ta bayyana dalilin da ya sa har yanzu ba ta kai tsohon gwamnan Kaduna,...

Wanene sabon Shugaban Rundunar ‘Yan Sandan Nijeriya, Olatunji Disu?

AIG Olatunji Disu ya kasance gogaggen jami’i wanda aka nada don jagorantar rundunar 'yan sandan kasar a matsayin IGP na 23. A cewar fadar shugaban...

Mafi Shahara